BINTUS-SUNNAH

@bintussunnah


Domin Faɗakarwa da Tunatarwa Zuwa Ga Al'ummah Ta Fannoni Daban-Daban.

TELEGRAM:
https://t.me/BINTUSSUNNAH

FACEBOOK:
http://www.Facebook.com//Bintusunnah/

YouTube:
https://youtube.com/channe

WHATSAPP:
http://api.whatsapp.com/send?phone=+2349030947171

BINTUS-SUNNAH

23 Oct, 11:26


20/RABI'UL THANI/1446
23/OCTOBER/2024

ADDU’AR YAU LARABA:
Ya ALLAH ka taimaki musulunci da musulmai a duk inda suke, ka karya kafurci da azzalumai a duk inda suke.

HADISIN YAU LARABA:
Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce: “Wata ƙungiya daga cikin al'ummata ba za ta gushe ba tana kan gaskiya, Duk wanda ya wulaƙanta su ba zai cutarda su ba, har zuwa sanda lamarin ALLAH zai zo.” [Muslim ya ruwaito shi]

Telegram
https://t.me/BINTUSSUNNAH

Facebook
http://www.Facebook.com//Bintusunnah/

BINTUS-SUNNAH

22 Oct, 10:27


19/RABI'UL THANI/1446
22/OCTOBER/2024

ADDU’AR YAU TALATA:
Ya ALLAH ka gafarta mana zunubanmu ka azurtamu da kyakkyawan ƙarshe.

HADISIN YAU TALATA:
Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce: “Zamanin zai kusanto (zai rinƙa sauri), ayyuka za su ragu (na alkhairi cikin mutane) za'a sanyawa mutane tsananin rowa, kuma 'ALHARAJ' zai yawaita. sahabbai suka ce, menene ALHARAJ ya Manzon ALLAH? sai yace shine Kashe-Kashe (kisa ko ina).” [Bukhari: 6688, Muslim: 4956]

Telegram
https://t.me/BINTUSSUNNAH

Facebook
http://www.Facebook.com//Bintusunnah/

BINTUS-SUNNAH

21 Oct, 11:18


18/RABI'UL THANI/1446
21/OCTOBER/2024

ADDU’AR YAU LITININ:
Ya ALLAH ka sanya alkhairi a cikin ƙuruciyarmu da tsufanmu kasa mu amfani kanmu da al'ummarmu a tsawon rayuwarmu.

HADISIN YAU LITININ:
Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce: “Mafi sharrin mutane, shi ne wanda rayuwarsa ta yi tsawo, kuma aikinsa ya yi muni.” [Tirmidhi: 2330]

Telegram
https://t.me/BINTUSSUNNAH

Facebook
http://www.Facebook.com//Bintusunnah/

BINTUS-SUNNAH

20 Oct, 11:38


17/RABI'UL THANI/1446
20/OCTOBER/2024

ADDU’AR YAU LAHADI:
Ya ALLAH ka kyautata mana harsunan mu ka tsare mu daga gulma da binciken abinda bai shafe mu ba.

HADISIN YAU LAHADI:
Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce: “Ya Ku taron waɗanda suka yi Imani da harshensu, amma imani bai shiga zuciyarsu ba, Kada ku rinƙa yin gulmar musulmi, Kuma kada ku rinƙa bibiyar al'aurar su, domin duk wanda yabi al'aurar su, shi ma ALLAH zai bi tasa al'aurar, duk kuwa wanda ALLAH ya bi al'aurar sa, ALLAH zai kunyata shi a cikin gidansa.” [Abu-dawud ya ruwaito shi, Albany ya Inganta shi]

Telegram
https://t.me/BINTUSSUNNAH

Facebook
http://www.Facebook.com//Bintusunnah/

BINTUS-SUNNAH

19 Oct, 22:14


FAT-HUL MAJEED SHARHU KITABIT-TAUHEED //89

CETO DA ZA A YI A LAHIRA IRI SHIDA (6) NE:

1● Babban ceto da Manyan Annabawa zasu ja da baya wajen nema, Annabi (ﷺ) zai ce shi zaiyi, shi kaɗai ke samo ceton nan.

2● Ceto ƴan Aljannah su shige ta.

3.● Ceton masu zunubai da za a sa a wuta kar su shiga.

4● Ceton masu zunubai da suke wuta a fito dasu.

5● Ceto a cikin Aljanna a ƙara ma wasu matsayi da daraja.

6● Ceton Baffan Manzon ALLAH (ﷺ) Abu ƊALIB domin sauƙaƙa masa azaba za a fito dashi saman wuta a samasa takalman wuta.

-Sheikh Salih AlFauzan (Hafizahullah)

https://t.me/BINTUSSUNNAH

BINTUS-SUNNAH

19 Oct, 14:40


ثَمَانِيَةٌ تَجرِي عَلَى النَّاسِ كُلِّهِم
وَلا بُدَّ لِلإِنسَانِ يَلقَى الثَّمَانِيَهْ

سُرُورٌ وَحُزنٌ وَاجتِمَاعٌ وَفُرقَةٌ
وَيُسرٌ وَعُسرٌ ثُمَّ سُقمٌ وَعَافِيَه

BINTUS-SUNNAH

19 Oct, 09:27


16/RABI'UL THANI/1446
19/OCTOBER/2024

ADDU’AR YAU ASABAR:
Ya ALLAH ka bamu rinjaye da imani da aminci da musulunci da nasara akan abin da kake so kuma ka yarda  dashi.

HADISIN YAU ASABAR:
Daga Abdullahi Ɗan Abbas (RA) Ya ce: Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce da shi: “Ya kai yaro: Zan sanar da kai wasu maganganu; Ka kiyaye ALLAH zai kiyaye ka, Ka kiyaye ALLAH za ka tarar da shi gaba gare ka Idan za ka roƙa, ka roƙi ALLAH, Idan za ka nemi taimako ka nemi taimakon ALLAH, Ka sani da a ce Al'umma za ta haɗu a kan ta amfane ka da wani abu, ba za su amfane shi da komai ba, sai abinda ALLAH ya rubuta gare ka, Da kuma za su haɗu a kan su cutar da kai da wani abu, ba za su iya cutar da kai da komai ba, sai da abinda ALLAH ya rubuta a Kara, An ɗage Alƙaluman, Takardun sun bushe.” [Tirmizi da Ahmad suka ruwaito shi]

Telegram
https://t.me/BINTUSSUNNAH

Facebook
http://www.Facebook.com//Bintusunnah/

BINTUS-SUNNAH

18 Oct, 11:51


Shin kuna yin wasu daga cikin waɗannan kusakuran a ranar Juma'a?!!!

BINTUS-SUNNAH

18 Oct, 08:54


15/RABI'UL THANI/1446
18/OCTOBER/2024

ADDU’AR YAU JUMA'A:
Ya ALLAH ka ƙara salati ga Manzon tsira (ﷺ) da iyalansa da sahabbansa da waɗanda suka yi imani suka kyautata halayensu har izuwa ranar al-ƙiyamah.

HADISIN YAU JUMA'A:
Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce: “Haƙiƙa ALLAH Yana da wasu mala'iku masu yawo a bayan ƙasa, suna isar min da saƙon gaisuwar al'mmatah a gare ni.” [Nasa'i Ya ruwaito shi]

TELEGRAM:
https://t.me/BINTUSSUNNAH

FACEBOOK:
http://www.Facebook.com//Bintusunnah/