16/RABI'UL THANI/1446
19/OCTOBER/2024
ADDU’AR YAU ASABAR:
Ya ALLAH ka bamu rinjaye da imani da aminci da musulunci da nasara akan abin da kake so kuma ka yarda dashi.
HADISIN YAU ASABAR:
Daga Abdullahi Ɗan Abbas (RA) Ya ce: Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce da shi: “Ya kai yaro: Zan sanar da kai wasu maganganu; Ka kiyaye ALLAH zai kiyaye ka, Ka kiyaye ALLAH za ka tarar da shi gaba gare ka Idan za ka roƙa, ka roƙi ALLAH, Idan za ka nemi taimako ka nemi taimakon ALLAH, Ka sani da a ce Al'umma za ta haɗu a kan ta amfane ka da wani abu, ba za su amfane shi da komai ba, sai abinda ALLAH ya rubuta gare ka, Da kuma za su haɗu a kan su cutar da kai da wani abu, ba za su iya cutar da kai da komai ba, sai da abinda ALLAH ya rubuta a Kara, An ɗage Alƙaluman, Takardun sun bushe.” [Tirmizi da Ahmad suka ruwaito shi]
Telegram
https://t.me/BINTUSSUNNAH
Facebook
http://www.Facebook.com//Bintusunnah/