کانال Sheikh Abdullahi Dahiru 📚 @tambayamabudinilimi در تلگرام

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚
Mai Sha'awan Samun Karatun,Fiqihu,Aqida
Koyon Larabci, Ilimin Sarfu, Nahawu, Balagha Dakoyon Rubutun Larabci, .....
Kasance Da Wannan Shafi Dayardan Zaisamu Abunda Yake Buqata.
4,196 مشترک
271 عکس
140 ویدیو
آخرین به‌روزرسانی 09.03.2025 13:35

کانال‌های مشابه

Awaitors of Mahdi (a.s)
3,303 مشترک
The Leader
2,400 مشترک

Sheikh Abdullahi Dahiru: Jagoran Ilimi a Fannin Addini da Harshe

Sheikh Abdullahi Dahiru na daya daga cikin manyan malaman addini a Najeriya, wanda ke taka muhimmiyar rawa wajen bayar da ilimi mai inganci ga matasa a fannoni da dama. Tare da tsawon shekaru na koyarwa, Sheikh Abdullahi ya zamo sanannen malami a fannonin Fiqihu da Aqida, wanda ya shahara wajen koyar da ilimin Larabci da sauran zamantakewa tare da hanzarta koyo da kuma koyarwa. A cikin wannan makala, zamu duba irin tasirin da Sheikh Abdullahi ke da shi a cikin al'umma da kuma yadda yake taimaka wa matasa wajen samun ingantaccen ilimi. Hakanan, za mu yi la’akari da wasu daga cikin tambayoyin da mutane ke yi game da iliminsa da hanyoyin koyarwarsa, domin samar da karin haske ga masu sha'awar wannan fanni.

Menene Fiqihu, kuma me ya sa yake da muhimmanci a cikin ilimin addini?

Fiqihu yana nufin ilimin shari'a na Musulunci wanda ke tantance dokokin da suka shafi rayuwar al'umma. Wannan fanni yana da matukar muhimmanci saboda yana ba da damar fahimtar abin da ya dace a yi ko a guje wa a cikin al'amuran yau da kullum, daga ibada har zuwa mu'amala. Malamai kamar Sheikh Abdullahi Dahiru suna taka muhimmiyar rawa wajen bayyana wannan ilimi ga al'umma, ta yadda zasu iya gudanar da rayuwarsu bisa ga koyarwar addini.

Haka kuma, Fiqihu ya na da matukar tasiri wajen karfafa zaman lafiya a cikin al'umma. Lokacin da mutane suka san hakkin su da wajabinsu a cikin shari'a, hakan na taimakawa wajen rage rikice-rikice da tasiri mai kyau a cikin al'umma. Malamai kamar Sheikh Abdullahi suna da rawar da suke takawa wajen ilmantar da mutane, ta hanyar shirya taruka da koyar da dakin karatu.

A wane fanni ne Sheikh Abdullahi Dahiru ke bayar da horo a ilimin Larabci?

Sheikh Abdullahi Dahiru yana bayar da horo a fannin ilimin Larabci wanda ya hada da nahawu, sarfu da balagha. Koyon Larabci yana da matukar muhimmanci ga wadanda suke son samun ingantaccen ilimi game da addinin Musulunci, domin yawancin littattafan ilimin addini, da hadisi, da Qur'ani ana rubuce su ne cikin harshen Larabci. Hakan ya sa Sheikh Abdullahi ke ganin bukatar koyar da wannan fanni ga matasa da kewayen gidajen karatu.

Hakanan, ilimin Larabci yana ba da damar samun fahimta mai zurfi game da koyarwar addini da al'adun Musulunci. Malamai kamar Sheikh Abdullahi suna kira ga matasa da su rungumi ilimin Larabci a matsayin hanya ta cimma zurfafa fahimta a fannonin addini da zamantakewa, wanda hakan zai inganta rayuwarsu.

Ta yaya Sheikh Abdullahi ke taimaka wa matasa wajen samun ingantaccen ilimi?

Sheikh Abdullahi yana nuna himma wajen zayyana shirye-shiryen horo da za su taimaka wa matasa wajen samun ingantaccen ilimi. Ya na shiryawa matasa karatuttuka, inda suke koyon muhimman darussan addini da na zamantakewa. Haka ne ma, yana ba da damammaki ga matasa su shiga cikin dandalin tattaunawa inda zasu iya tambayar duk abin da ke damunsu ko kuma samun karin bayani kan abubuwan da suka koya.

Bugu da kari, Sheikh Abdullahi yana amfani da kafafen sada zumunta wajen yada ilimi da shawarwari ga matasa. Hakan yana sa su iya samun ilimi daga ko ina cikin duniya. Ta wannan hanyar, ana kara fadada yawan matasan da suka shafi karatun addini da ingantaccen ilimi na zamani.

Me yasa koyon Larabci ke da matukar muhimmanci ga muslmi?

Koyon Larabci yana da matukar muhimmanci ga Musulmi saboda harshen Larabci ne aka rubuta Qur'an da Hadisai. Samun ilimin Larabci na ba Musulmi damar karanta da fahimtar ayoyin Qur'ani da Hadisai a asalin harshensu, wato tare da hakikanin ma'anoni. Hakar tana ba da haske da inganci wajen gudanar da ibada da sauran al'amuran rayuwa.

Haka zalika, koyon Larabci yana taimaka wa Musulmi su fahimci al'adun Musulunci da kuma tsarin rayuwar da aka gina bisa ga shari'a. Wannan yana karfafa alakar Musulmi da addininsu da kuma ba su damar gudanar da al'amuransu cikin tsari daidai da koyarwar addini.

Menene Aqida, kuma ta yaya take shafar rayuwar Musulmi?

Aqida na nufin imani a cikin Allah da abubuwan da suka shafi addini. Wannan yana dauke da akidun da suka shafi imani, kamar imanin da ga Allah, mala'iku, littattafai, annabawa da ranar lahira. Aqida tana daga cikin ginshikan addinin Musulunci, kuma tana da matukar tasiri kan yadda Musulmi ke gudanar da rayuwarsu.

Rayuwa ba tare da Aqida ba na iya haifar da rudani da rashin tabbas a cikin al'umma. Malamai kamar Sheikh Abdullahi suna daukar nauyin ilmantar da matasa kan Aqida, don su sami tushen da ya dace na addini wanda zai ƙarfafa musu gwiwa da kuma juriya a dukkan fannonin rayuwarsu.

کانال تلگرام Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

Tambayamabudinilimi channel, managed by Sheikh Abdullahi Dahiru 📚, is a treasure trove of knowledge for those interested in learning about various aspects of Islamic studies. From Fiqh and Aqida to Arabic grammar, language, rhetoric, and writing, this channel covers a wide range of topics essential for anyone seeking to deepen their understanding of the Islamic faith and its teachings. Whether you are a beginner looking to start your journey in Islamic education or an advanced student wanting to enhance your knowledge, Tambayamabudinilimi has something for everyone. Join us on this enlightening journey as we explore the depths of Islamic knowledge and learn from the wisdom shared on this platform. Don't miss out on this opportunity to expand your horizons and grow in your faith. Kasance Da Wannan Shafi Dayardan Zaisamu Abunda Yake Buqata!

آخرین پست‌های Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

Post image

MAS,ALOLIN DASUKE KARYA AZUMI 04.[ DARASI NA 08 ].

14, baya halatta mutum yahaɗiye kaki ko wani abun dayariga yafito bakinsa, bisa ihtiyaɗi na wajibi.
Idan kuma yahaɗiye ba bisa zaɓinsaba ko bisa Mantuwa azuminsa bai karyeba,
Amma yawun dayake bakinsa bamatsala dan mutum yahaɗiye shi.

15, Anfani da abun fesawa na masu ciwon sarƙewan nunfashi da makamantan sa domin ya buɗa magudanan nunfashi ko sauƙaƙe numfashi ba matsala kuma baya karya azumi.

16, Ɗure da akeyiwa mutum tawajen bayan garinsa ( masu ciwon rashin iya bayan gari ko ciwon ciki .... ) inda abu me ruwa ruwa ne yana karya azumi koda kuwa dole takama ayi hakan.
Amma inda daskarer_rene bamatsala baya karya azumi.

17, Idan Me Azumi yaƙirƙiro amai da gangan azuminsa yakarye,
Kodakuwa dolene tasashi yin aman saboda ciwo ko wani abun daban,
Amma idan yayine bisa Mantuwa kokuma kuskure ba bisa zaɓinsaba azimin sa bai karyeba.

18, bisa ihtiyaɗi na wajibi ; Wajine ma azumi yanisanci Anfani da Allura me ƙara ƙarfin jiki dama wasu abubuwan da,ake sawa ta jijiya hakanan ruwan asibiti ( Drip ) da dukkan nau,o'insa.
Amma Allura Da akeyi bana jijiyaba saboda jinyan rashin lafiya bata karya azumi haka alluran dake kashe zafin wajen da za ayi ɗinki ko aiki itama bata karya azumi.

19, Bamatsala mutun yanaķalto Ruwayoyin dasuzo daga Manzon Allah (s,a,w) ko iyalan gidansa wanda aka rawaitosu a littatafai wanda mutum baida masaniya akan cewa ķarya akayiwa ma,asumi.
Dukda cewa bisa ihtiyaɗi na Mustahabbi mutum yajingina ruwayan zuwaga littafin daya dauko aciki baya jinginawa ma,asumi kai tsayeba.

20, Idan Mutum yanaƙalto magana yajinginawa Allah (s,w,t) ko Manzon Allah (s,a,w) ko wani daga cikin ma,asumai, yanada Qudurin cewa ya inganta, sedaga baya seta bayyana masa cewa bai ingantaba azuminsa bai lalaceba.

21, wajibine mutum mai azumi yanisanci haɗiye ƙura mai kauri, bisa ihtiyaɗi na wajibi,
Kamar ƙuran dake tashi lokacin Shara ko kuma wanda iska ke tayarwa,
Idan Mutum bai nisanci ƙuran ba har yashige maƙogoronsa to azuminsa yakarye bisa ihtiyaɗi na wajibi.

22, Idan Mutum yamanta cewa yana azumi sai bai nisanci ƙuraba har yashige maƙogoron sa Azumin sa bai lalace ba,
Haka hukuncin yake Idan ƙuran yashige batareda zaɓinsaba.

23, Haɗiye Jinin daya fito daga dasashi ( dasori ) Baihalatta,
Wajibine mutum yatofar dashi, yana tofarwa kuma bakinsa ya tsarkaka ba dole saiya kurkureba,
Amma wannan Idan yazama jinin bai ɓace acikin yawuba kenan - ta yadda baza,aganshiba inda za atofar da yawun - amma idan yaɓace acikin yawuto ya tsarkaka ya halatta ahaɗiyeshi kuma Azumin mutum bai ɓaciba.

23, Bamatsala Mutum yatsaftace bakinsa da makilin da buroshin, matuƙar mutum bai haɗiye wani abu da gangan ba.
Jiƙa jiki da ruwa tahanyan shiga cikinsa ko she ƙashi akan mutum ko wanka a ƙarqashin shaya duk basu ɓata azumi.


Abdullahi Dahiru

https://t.me/TAMBAYAMABUDINILIMI

09 Mar, 13:22
9
Post image

MAS,ALOLIN AKAN ABUBUWAN DASUKE KARYA AZUMI.
(Darasi Na 06)

1, Abubuwan da aka anbata abaya masu karya azumi inka cire janaba duka suna karya azumine in aka aikatasu da gangan ba bisa sha,afa ko mantuwaba.
Misali : Damutun zaici abinci ko yasha abunsha bisa Mantuwa azuminsa bai ɓaciba,
Babanbanci akan Azumin wajibi dana Mustahabbi.

2, Damutum Zai aikata ɗaya daga acikin abubuwa masu karya azumi bisa Mantuwa, sai ya sake aikatawa dan gangan saboda tunanin cewa ai lokacin daya aikata bisa Mantuwa azuminsa ya ɓaci to wannan aikatawa na biyun yaɓata masa Azumi.

3, Damai azumi zaiyi shakka akan cewa azuminsa ya lalace ko bai lalace ba,
misali : yayi shakka akancewa shin lokacin daya kurkure baki ya haɗiye yawu shin akwai ruwan daya shige ciki ko babu to anan azuminsa yana nan bai ɓaciba.

4, Bai halattaba ( haramunne ) yin buɗa baki kafun samun yaqinin cewa dare yashiga,
Damutum zai aikata hakan to zai biyawannan Azumin Bayan sallah kuma sai yayi Kaffara, Koda Kuwa bashida tabbacin cewa lokacin dayasha rana ne, ( rashin wancan yaqinin nafarko shizai lizimta masa Kaffara da kuma biyan azumin)

5, Idan Mutum yana shakkan cewa shin Alfijir Yaketo ko bai keto ba, bawajibi bane saiya bincika domin samun tabbaci kafun yasha ruwa ko yaci abinci,
Amma damutum zai sha ruwa ko yaci abinci batareda bincikeba sedaga baya yazama sai daga baya ta bayyana cewa lokacin dayaci abincin ko yasha abunsha Alfijir yaketo,
To wajibine yakame yakai wannan aranan kuma zai biya Azumin Bayan sallah saidai ba kaffara akansa.

6, Idan Mutum yana shakkan cewa Alfijir yaketo ko bai ketoba sai yayi bincika ta tabbata masa Alfijir be ketoba sai yaci abinci koyasha abunsha sai daga baya ta bayyana masa cewa ashe lokacin dayaci abincin ko yasha abunshan Alfijir yaketo, dukda haka Azuminsa yananan bai ɓaciba.
Amma wannan maganan akan Azumin watan Ramadanne, amma wanda bashiba yana azumi na ɓacine kaitsaye daga Mutum ya aikata abunda ke karya azumi baya Alfijir.

📚mas,ala ta 668 zuwa 673.

7, Yahalatta ga mace tasha maganin Dazai hana jinin haila zuwa ko ya jinkirta zuwansa domin tasamu daman yin azumin watan Ramadan cikekke batareda tasha Azumi saboda hailaba, matuqar shan maganin bazai cutar da ita cutarwa mai tsanani ba, ya halatta.

8, Idan Me Azumi yanitsar da kansa acikin zuwa dagangan azuminsa yakarye bisa ihtiyaɗi na wajibi,
Wajibine yabiya bashin wannan Azumin Bayan sallah.
Idan kuma me Azumi yashiga ruwa seyake shakka cewa shin ruwa shin kansa yanitse duka kobenitse ba to Azumin sa nanan be karyeba.

9, Idan Me Azumi yanitsar dakansa cikin ruwa bisa kuskure batareda zaɓinsa ba azuminsa nanan, sede wajibine Alokacin yacire kansa daga cikin ruwan da gaggawa.
Kuma haka hukuncin yake Idan Mutum yamanta yanitsar dakansa cikin ruwa Azumin sa bai karyeba.

10, Bisa ihtiyaɗi na wajibi ; Wajibine ga amai Azumi Yanisanci shaye_shaye dadukkan Mabanbantan nau,o'insa,
Hakanan abubuwan dasuke bugarwa wanda ake sawa ta hanci,
Dama waɗanda ake sawa aqasan harce.

11, Idan Mutum Yayi gyasa sai abinci yafito bakinsa bai halatta ya haɗiye shiba,
Hakanan bai halatta mutum yahaɗiye sauran abinci daya maƙale abakinsa ba,
Idan yahaɗiye abincin batareda zaɓiba bisa kuskure azuminsa nanan,
Amma idan yahaɗiye dagangan to Azumin sa yakarye.

12, Idan Mutum ya ankara lokacin dayakecin abinci cewa Alfijir yaketo wajibine yafidda abunda ke bakinsa na abinci,
Amma idan mutum yacigaba to azuminsa yakarye.

13, Yahalatta ga amai Azumi yaɗanɗana abinci ko tattaunashi wa yara ko Tsuntsaye, Hakanan tauna Cingam kodakuwa yaji ɗanɗanon a bakinsa,
saidai dasharaɗin karya haɗiye komai daga cikinsa,
Amma Idan wani abu yakuɓuce yashige batareda zaɓinsa ba Azuminsa na nan bai karyeba.

Abdullahi Dahiru

https://t.me/TAMBAYAMABUDINILIMI

09 Mar, 13:11
17
Post image

YADDA AKE ITTIKAFI DA HUKUNCIN SA.02

8, Ya Halatta afita daga masallaci imyazama akwai laruran databijirowa mutum idan yazama larurar data sameshin ahankalce ko a Shari,ance ko bida al,ada Dolene Mutum yafita yakauda wannan laruran, kamar zuwa bayi dan biyan buqata ko wanka, ko bada sharda akan wani al,amari mai muhimmanci, gaida mara lafiya, raka mamaci, damakamanta nsu, amma wajibine a dukkan wuraren mutum yataƙaita akan abunda larura ya hukunta.

9, Yahalatta Mutum ya yanke ittikafi arana na biyu kafun yacika kwana biyu cif, amma idan yacika kwana biyu wajibine yaƙariso na uku, ittikafin Bakance idan ayya nanne ne ( mutum ya ayyana wasu ranakun kamar sha uku Shahuɗu Shabiyar amatsayin ranakun ittikafin sa.) To anan bai halatta mutum ya yankeshi ba inde yafara, amma idan ba ayyananne bane hukuncinsa Hukuncin ittikafin Mustahabbi Ne (a biyun farko ya halatta ayanke kafun acika kwana biyu amma in ancika kwana biyu wajibine aƙarisa uku.)

10, Idan ittikafin yaro zai zamo silan cutuwan mahaifinsa ko mahaifiyarsa to wajibine yanemi izininsu kafun yashiga, Mustahabbi Ne ma yanemi izininsu koda baxai cutar dasuba bisa ihtiyaɗi.

11, Haramunne ga mai ittikafin saye da sayarwa ( kasuwanci ) dakuma jayayya idan yakasance domin yin nasara da bayyana Fifiko, dakuma shaƙan abubuwa masu ƙamshi danufin jin daɗi.

12, idan mutum ya ɓata ittikafinsa na wajibi, Idan ittikafin ayananne ne wajibine yabiyashi, amma idan wajibinda ba ayyananne bane wajibine yasakeshi akaro nagaba, (ana farko niyyan ramuwa zaiyi saɓanin na biyu niyyan zuwa dashi zaiyi ba ramako ba.)

12, Idan Mutum yaɓata ittikafin Mustahabbi bayan yacika kwana biyu wajibine yabiyashi, amma Dazai ɓatashi arana nafarko ko na biyu kafun cika kwana biyu to ba wajibine yabiya ba.

13, biyan ittikafi ko sake ittikafi yana wajaba ne (wanda akayi magana akansu amas,alolin baya) idan yazama cewa mutum bai sharɗanta yanke ittikafin inwani abu yabijiro masa ba lokacin niyya,
( amma inya sharɗanta to ko wani abun yabijiro masa ya yanke to ba dole bane yabiya ko yasake )

14, kaffaran ɓata ittikafi kamar kaffaran karya Azumin watan Ramadan da gangan ne, wanda shine ƴanta wuya, Azumin wata Biyu ajere, ciyar da miskinai sittin.

Abdullahi Dahiru

https://t.me/TAMBAYAMABUDINILIMI

09 Mar, 12:56
20
Post image

YADDA AKE ITTIKAFI DA HUKUNCIN SA.

1, Ittikafi Mustahabbi ne.
Ittikafi shine : Tarewa a masallaci a masallaci domin bautan Allah.
ya inganta mutum yayi ittikafi akowani lokaci, amma lokaci dayafi shine watan Ramadan musamman goman ƙarshe na watan Ramadan, Sharaɗin Ingancin ittikafi shine yazama mutum yana azumi sannan kar ittikafi yagaza kwana uku ajere tareda dararen dake tsakanin kwanakin.

2, Sharaɗin ittikafi ne Mutum Yayi niyyah sannan kuma yayi niyyan kusantan Allah maɗaukakin sarki da wannan aikin da zaiyi, abunnufi yakasance zaman damutum zaiyi a masallacin domin kusantan Allah maɗaukakin sarkine Kaɗai, karya cakuɗashi dakowani irin nau,in riya da nuna kai amatsayin mai ibada.

3, ya halatta gamai ittikafi ya sharɗamta tun alokacin niyyansa cewa zai iya yanke wannan ittikafin idan wani abun yabijiro masa zai fita daga masallacin koda kuwa ra ta uku ce na ittikafin sa.

4, ittikafi ya halatta akowani masallacin dayazama ana dukkan sallolin musulunci aciki, mafifitan masallatai damutum zaiyi aciki guda Huɗu Ne, masallacin makka (inda ka,aba taje), masallacin madina (inda manzo -s,a,w- yake ) masallacin kufa, masallacin basrah,
Amma sauran masallatai waɗanda ba duka salloli akeyi acikiba, wanda ana sallan Jam'i aciki kuma sunada limami Adali, ya inganta mutum yayi ittikafi aciki, amma da niyyan kusantan Allah maɗaukakin sarki ( batareda ayyana cewa Mustahabbi bane ) kawaide dafatan Allahyakarɓa masa.

6, wajibine ittikafi kar yagaza kwana uku ajere, Yahalatta Mutum ya yankeshi kafun yacika kwana biyu cif, amma idan yacika kwana biyu to wajibine yaƙariso na ukun, bamatsala mutum yayi sama da kwana uku koda kuwa mutum yaƙara kwana ɗaya ne ko dare ɗaya, ƙari bashida iyaka ayyananne, saidai bayan Mutum yacika kowani ƙarin kwana biyu to ya wajaba yazoda na uku.

7, Shariɗine a ittikafi yazama mutum yatare gaba ɗaya a masallacin batareda Yana fitaba, da mutum zai fita dagangan bisa zaɓinsaba ittikafin sa ya lalace inde ba,a wuraren daya halatta afita bane, kodakuwa baisan wannan Hukuncin Ba (cewa ittikafin sa yalalace din).

✍️ Abdullahi Dahiru

https://t.me/TAMBAYAMABUDINILIMI

08 Mar, 21:59
118