A wannan halin da al'ummar wannan ƙasa suke ciki dama sauran ƙasashen musulmai ahir ɗinka da kare azzulmai da ƙoƙarin ba su uzuri da mafaka, da ma yi wa wani fata ko murnar samun wani matsayi a cikinsu. Don kuwa duk muguwar addu'ar da ake musu, da kuma zaluncin da suke yi to kana da kaso a ciki.
Abubakr al-Mirwazi ya ce lokacin da aka ɗaure Ahmad bn Hanbal, sai mai gadin kurkukun ya tambayesa : Shin hadisin da aka ruwaito game da azzalumai da masu taimaka musu sahihi ne?" Sai Imam Ahmad ya ce: "Eh." Mai gadin kurkuku ya ce: "To, shin ni ina daga cikin masu taimaka wa azzalumai ?" Sai Imam Ahmad ya ce: "Masu taimaka wa azzalumai su ne masu aske maka gashinka, masu wanke maka kaya, masu dafa maka abinci, masu saye da sayarwa da kai, amma kai kanka kana daga cikin azzalumai."
Iya wannan kaɗai ya isa nuna maka hatsarin azzalumi da taimakonsa.
Allah ya sassauta mana ya kuma yi mana maganin azzalumai a duk inda suke.