Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

@tambayamabudinilimi


Mai Sha'awan Samun Karatun,Fiqihu,Aqida
Koyon Larabci, Ilimin Sarfu, Nahawu, Balagha Dakoyon Rubutun Larabci, .....
Kasance Da Wannan Shafi Dayardan Zaisamu Abunda Yake Buqata.

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

21 Jan, 00:21


أفسحوا لـِ سـورة الكهف وقتـاً في يومكم ثمة نور يحفكم لا ينطفئ🤍🌱.

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

21 Jan, 00:16


يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا مَن يَرْتَدَّ مِنكُمْ عَن دِينِهِ فَسَوْفَ يَأْتِي اللَّهُ بِقَوْمٍ يُحِبُّهُمْ وَيُحِبُّونَهُ أَذِلَّةٍ عَلَى الْمُؤْمِنِينَ أَعِزَّةٍ عَلَى الْكَافِرِينَ يُجَاهِدُونَ فِي سَبِيلِ اللَّهِ وَلَا يَخَافُونَ لَوْمَةَ لَائِمٍ ۚ ذَٰلِكَ فَضْلُ اللَّهِ يُؤْتِيهِ مَن يَشَاءُ ۚ وَاللَّهُ وَاسِعٌ عَلِيمٌ (54)

عن مالك بن أنس عن ابن عمر عن عمر بن الخطاب قال: قال رسول الله يوم خيبر:
«لأعطينَّ الراية غداً رجُلا يحبّ الله ورسوله ويُحبّه الله ورسوله كرَّار غير فرَّار يفتح الله عليه، جَبرئيل عن يمينه وميكائيل عن يساره» . فبات المسلمون كلّهم يَستشرفون لذلك، فلمّا أصبَحَ قال: «أين علي بن أبي طالب؟» قالوا: أَرمد العين . قال: «آتوني به»، فلمّا أتاه قال رسول الله: «ادنُ منّي» . فدَنى منه فتفل في عينيه ومسحهما بيده فقام علي بن أبي طالب من بين يديه وكأنهُ لم يرمَد، وأعطاه الراية، فقَتَل مرحب وأخذ مدينة خيبر .

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

21 Jan, 00:03


Wuraren Da Iran ta shirya kaiwa hari idan Isra'ila tayi kuskuren kaimata hari dasunan ramuwa.

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:56


💥🔥🔥🔥💥

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:56


💥🔥💥🔥💥saqon iran ya isa.

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:56


Gani ya koriji 💥💥💥

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:56


Alhamdulillahi


Iran tafaranta ran muminai kamar yadda tasaba

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:56


Anyi bikin buɗe hauza mai dauke da sunan Shugaban shahidan muqawama Say yid Has san Nas rullah.

https://t.me/TAMBAYAMABUDINILIMI

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:55


TAFIYA GAMAI AZUMI A WATAN RAMADAN.[Darasi na 10]

1, Bai Inganta Matafiyi Yayi azumiba a watan Ramadan inde tafiyansa yakai ƙasaru, Saida awasu wurare keɓantattu.

2, Yahalatta Mutum Yayi tafiya awatan Ramadan koda kusa sanadin tafiyan shine yanasone karyayi Azumin wannan ranan, Saida yasani zaiyi mummunan Asara na lada mai girman gaske.

3, Makaruhine ga Matafiyi bama shikaɗaiba duk wani wanda Yahalatta yasha Azumi makaruhine yacika cikinsa Yayi ɗif da abinci koda abinsha, Hakanan saduwa da iyali.

4, Idan mai azumi yayi niyyan tafiya kafun zawali,
Idan yayi niyyan tafiyanne tun cikin dare zaisha azumi ( amma ba agida ba sai yaje Haddut-tarakh-khus) inganta yayi wannan Azumin ba.
Amma in yayi niyyan tafiyanne bayan ketowan Alfijir wajibine yakai wannan Azumin Kuma zai biyashi bayan sallah bisa ihtiyaɗi na wajibi.

5, Bai halattaba ga mai azumin da zaiyi tafiya kafin zawali yaci abinci ko yasha abinshaba harsai ya fita a garinsu ya wuce Haddut-tarakh-khus,
Dazai Ci abinci ko yayi wani abunda ke karya azumi kafun yakai can to wajibine yabiya wannan Azumin Bayan sallah kuma saiyayi Kaffara bisa ihtiyaɗi na wajibi,
Saidai Idan yazama baisan Hukuncin bane kokuma ya gafala ne daga hukunci to anan bazaiyi Kaffara ba.

6, idan mai azumi yayi niyyan tafiya bayan zawali to bai halatta ya sha azumiba zai ƙarisa Azumin sa kuma zaiyi ķasaru a sallan sa.

7, Idan Matafiyi yadawo garinsu inya iso bayan shigan lokacin sallah Azahar To bashida wannan Azumin zai biya bayan sallah,
Amma idan ya iso kafin shigan lokacin sallah ne to wajibine ya sabunta niyyah yayi azumin wannan ranan,
inde bawai yariga Yayi Wani abunda zai Karya masa Azumi bane tun yama halin tafiya, inkuma yayi to bamaganan azumi zaide biya bayan sallah.


Abdullahi Dahiru

https://t.me/TAMBAYAMABUDINILIMI

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:53


JANABA DA HAILA [ 02 Darasi Na 09]

6, Yahalatta ga mai azumin da janaba tasameshi yayi bacci idan yana tsammanin cewa zai farka cikin dare yayi wanka,
Idan yayi bacci da niyyan zai tashi sai yamaka bai tashiba sai bayan fitowan Alfijir azuminsa ya inganta kuma bakomai akansa.
Amma Inda zaifarka cikin dare saiyaga cewa da sauran lokaci saiya koma bacci karona Biyu saibai farkaba har saida Alfijir yaketo, To wajibine yakame harzuwa shan ruwa, sannan daga baya zai biya wannan Azumin.

7, Wanda Janaba tasameshi Ko macensa haila yadauke mata saidai bazasu iya wankan tsarkiba saboda gudun ruwan zai cutar dasu kokuma babu ruwan, kokuma lokaci yaƙure ta yadda lokacin daya rage bazai isheshi wankaba, wajibine suyi taimama maimakon wanka,
Inkuma Mutum baiyi taimaman ba har Alfijir yaketo to bashida azumin wannan ranan kuma wajibine yakame a wannan ranan, sannan zai biya bashin wannan Azumin Bayan sallah kuma sai yayi Kaffara idan a watan Ramadanne.

8, Idan Mutum yana wankan tsarki da tunanin cewa wankan dayakeyi Ingancec_ce ne,
Saidaga baya tabayyana masa cewa ba daidai bane wankan dayakeyi, Azumin dayayi abaya ya inganta, saboda wanzuwansa da janaba badagangan bane,
Amma sallolinsa dayayi abaya wajibine yabiyasu dukka.

9, Idan Mace tamanta da wankan haila ko wankan nifasi na wani lokaci, sai daga baya ta Tuna, to azumin datayi tsawon wannan lokacin ya inganta, Babanbanci azumin Ramadanne ko wani azumin daban.

10, Idan Mutum yasan cewa idan yakusanci iyalinsa cikin azumi bazai iya wankaba saboda baruwa ko saboda wani uzurin nadaban, ya halatta duk da haka yakusanci iyalinsa sai yayi taimama maimakon wanka,
Amma idan baiyi taimamaba har Alfijir ya keto azumin sa ya lalace kuma dole yakame wanann ranan sannan bayan sallah zai biya wannan Azumin Kuma zaiyi Kaffara.

11, Idan Me azumi dagangan yayi wani abunda yasan cewa zai tayar masa da sha awa har Maniyyi yafita, kamar kallon ko taɓa abunda zai harfar da hakan koma wani abun daban, to azuminsa ya lalace.

12, Idan mai azumi yayi wanin daniyyan ya fidda Maniyyi, to koda Maniyyin bai fitaba zai qarisa wannan ranan kamar sauran masu azumi kuma zai biya wanann azumin bayan sallah bisa ihtiyaɗi na wajibi.

13, Idan mai azumi yafarka lokacin da baniyyi ke fita ajikinsa, bawajibi bane ya hanashi fita.

14, Idan Janaba tasamu mai mazumi ko yayi mafarki da Daddare, yaƙi wanka da gangan har lokacin wanakn yaƙure, Wajinine yayi taimama maimakon wankan, kuma zumunsa ya inganta, amma ya aikata haramun saboda rashin wankan dayayi.

14, Idan haila ko nifasi yabijirowa mace lokacin azumi acikin yini - bayan ketowan Alfijir ko da rana ko da yamma - azuminta ya lalace koda kuwa kafun Magriba ne da ƴan mintoci ne, zata biya wannan Azumin Bayan sallah,
Amma tabbas Allah zai bata ladan wannan azumi da tayi wanda bata samu daman ƙarisashiba.


Abdullahi Dahiru

Shiga nan domin samun audio na karatun 👇

https://t.me/TAMBAYAMABUDINILIMI

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:52


Sharhin Littafin Mujazul_Ahkam Hukunce Hukuncen Azumi.

Darasi Na shida. ((9))

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:51


ANKARARWA AKAN LABARIN ......

Maqiya Na anfani da yaɗa labarin cewa sayyid yayi shahadane domin sugano inda yake,
Dogara dacewa in labarin ya yaɗu za,ayita ƙiraye ƙirayen waya domin samun tabbacin gaskiya ne koba gaskiya to awannan lokacin sukuma sunada na,urori bibiyan wayoyin mutane atsakanin wayoyin tayuyu su samu bakin zaren wajen da yake,
Dan haka mukula da sharrin maƙiya bakowani labari bane zamu gaskata dan munji yana yawo,

Labari irin wannan daga wajen masu al,amarin zai fito saimu gaskata bawai kaji ance ba.

✍️ Abdullahi Dahiru

https://t.me/TAMBAYAMABUDINILIMI

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:51


Ɗaya Daga cikin makusantan sayyid h^san n^srull^h : - ya bada tabbacin cewa yana cikin qoshin lafiya.

"Dashi Zamuyi sallah Aqudus" !

https://t.me/TAMBAYAMABUDINILIMI

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:51


Alhamdulillahi
Labaru daga makusantan sayyid HSN NSRLLH sun tabbatar cewa yana halin lafiya.

Allah yaqara kariya yabamu nasara akan kafurai.


Abdullahi Dahiru

https://t.me/TAMBAYAMABUDINILIMI

Sheikh Abdullahi Dahiru 📚

20 Jan, 23:50


JANABA DA HAILA. [ 01 Darasi Na 08 ]

1, Idan Janaba tasamu mutum cikin azumi da Daddare kokuma mai haila ko mai jinin haihuwa tayi tsarki da Daddare, wajibine suyi Wankan tsarki kafun fitowan Alfijir,
Idan kuma sukaƙiyi da gangan har bayan fitowan Alfijir azuminsu ya lalace, kuma dole sukame da daga dukkan abunda ke karya azumi har lokacin ɓuɗa baki, sannan daga baya saisun biya wannan Azumin Kuma zasuyi Kaffara.

2, Idan Mutum mai azumi ya ankara bayan ketowan Alfijir cewa ashefa Janaba tasameshi tun cikin dare kokuma yayi mafarki darana Janaba tasameshi, duk azuminsu bai lalaceba, kuma ba wajibi bane mutum yagaggauta wanka daga zaran ya tuna.
Damutum zaisan cewa inyayi bacci zaiyi mafarki kuma Janaba zata sameshi ya halatta yayi baccinsa kuma koyayi mafarkin bakomai akansa azuminsa na nan.

3, ƙin yin wankan tsarki da gangan yana ɓata Azumin Ramadhan ne kawai dakuma biyan bashin sa ( ga wanda baisamu daman yi aramadan zai biya bayan sallah )
Amma sauran nau'o,in azumi kamar Azumin Bakance ko Azumin Nafila basu ɓaci dan mutum baiyi wanka ba har Alfijir ya fito.

4, wanda Janaba tasame shi cikin azumi Daddare saiya manta baiyi wanka ba har Alfijir yaketo azuminsa ya inganta na wannan ranan kuma bakomai akansa,
Amma idan mantuwansa yacigaba har yaqara wasu kwanaki to wajibine zai biya azumin waɗannan kwanakin,
Amma sallolinsa dukkan saiya rama tunna Ranan farko.

5, wanda Janaba tasameshi awatan Ramadhan, kokuma yafarka cikin dare yasamu kansa da Janaba, Idan yasa cewa idan yakoma bacci ba zai iya farkawa ba kafun fitowan Alfijir yayi wanka to "Haramunne" yakoma bacci kafun yayi wanka, Dazai koma bacci har Alfijir yaketo yana bacci baiyi Wanka ba to azuminsa ya lalace kuma wajibine yabiya wannan Azumin Bayan sallah kuma sai yayi Kaffara, kuma dole yakame awannan Ranan kamar sauran masu azumi.


Abdullahi Dahiru

Mai Bukatar Audio din darussan 👇

https://t.me/TAMBAYAMABUDINILIMI